Skip to main content

Posts

Ya kamata a dinga tabbatar da sahihancin labari kafin a yada - Sheikh Sabi'u Jibia

Sheikh Ibrahim Sabi'u ya yi kira ga 'yan Social Media da su dinga tabbatar da Ingancin labari kafin su yada shi. Mataimakin shugaban majalissar ta kungiyar JIBWIS dake tarayyar najeriya Sheikh (Barr) Ibrahim Sabi'u Jibia, a yayin da yake gabatar da khudbar sallar juma'a yayi kira  ga masu amfani da kafafen sadarwar zamani (Social Media) su guji yada sharri da labarin karya. Ya kara da cewa: yana da kyau mutane  su dinga bincike domin tabbar da ingancin labari kafin su yada shi don gudun aikata abinda zai sa mutum ya wayi gari yana mai ladama game da abinda ya aikata. Kazalika ya karanto ayoyi daga  alqur'ani mai girma da hadisan Annabi (S.A.W) wadanda suke magana akan haramcin yin irin wannan mummunan aiki, wanda yin haka babban abin kyama ne a wajen Allah madaukakin sarki. A cewarsa tsawon lokaci da ya gabata akan samu batagarin malamai ne masu karantar da hadisan karya a yayin da suke karantar da dalibansu, amma yanzu zamani ya canza, kana kwance a gida za kai ta ...
Recent posts

Yau shekara daya kenan da nada Sheikh Barr. Ibrahim Sabiu a matsayin "Sarkin Malaman Jibia"

Yau Lahadi 05/07/2020 Sheikh Barr. Ibrahim Sabiu ya yi shekara daya a matsayin "Sarkin Malaman Jibia". Tarihi ya nuna cewa tun farkon kafuwar masarautar Jibiya ba'a taba bada mukamin Sarkin Malamai ba sai a shekarar data gabata, inda aka dauko daya daga cikin Malaman da ke fadi tashi don ganin addinin Muslunci  ya samu gindin zama a fadin duniyar nan.  A shekarar data gabata ne, Mai girma Sarkin Arewan Katsina-Hakimin Jibia Alhaji Rabe Rabi'u Ibrahim, ya bada wannan mukami ga Malam Ibrahim Sabi'u, wanda akayi bikin nadin sarautar a ranar juma'a 05/07/2019 da misalin karfe 10 na safe, a fadar mai masarautar dake Jibiya. Barrister Ibrahim Sabi'u, ya kasance dan uwa na jini ga Sarkin Arewan Katsina-Hakimin Jibia Alhaji Rabe Rabi'u Ibrahim,  wannan alaka ta nuna cewa 'ya'yan wa da kanine, Sarkin Malamai yaya ne ga Hakimin na Jibiya.  An nada Sheikh Barr. Ibrahim Sabi'u a matsayin Sarkin Malamai ne biyo bayan kasancew...

AN ANNOUNCEMENT OF POSTPONED LECTURE - Masisja Nigeria

Sheikh Ibrahim Sabiu Jibia School    (MASISJA NIGERIA) On behalf of the leaders and members of the sect, is to inform the whole Muslim Ummah:  The Women's Question and Answer Lecture, by Sheikh Barr Ibrahim Sabiu Jibia, that will continue to present from Tomorrow and next week Saturday, has been postponed to some time.  This was followed by a statement from the Katsina State Government that the tuition in Islamic schools and Allo was suspended until the authorities allow them to continue their education. The leaders of the MASISJA have tried their best to secure of the next day and the next week, but it is also worth noting the instructions of the leaders, because obeying Allah and His Prophet and the Heads, and all that is needed to the Ummah, is one of the rights that hangs on a Muslim. But by the grace of Allah, any day this law is withdrawn, we will inform you on the day when the remaining remnants of the encampment will continue f...

A SHIRYE NAKE INYI MUQABALA DA KOWA DOMIN KARE MARTABAR MUSLUNCI - Sheikh Lawal Musa Jibia

Edin karamar sallar bana 1441/2020 da ya gabata, Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia mataimakin shugaban kwamtin Da'awah na kungiyar JIBWIS dake karamar hukumar Jibiya ta jihar Katsina, shine ya gabatar da wa'azi kafin isowar liman. A cikin nasihohinsa, ya janyo hankullan 'yan uwa musulmai da yi masu nasiha game da batanci da jifar da aka yiwa Mai girma sarkin musulmin najeriya a jiharsa ta Sokoto game da mas'alar ganin Wata, wanda hakan ya sabawa Shari'a ta addinin muslunci. Saboda haka ne wasu masu karancin karatu ke faman cecekuce domin a cikin nasihar ya bayyana masu irin wannan mummunan aiki a matsayin jahilai. Wannan dalilin ne yasa wasu tsiraru sukai tayi masa raddin jahilci suna yadawa a kafafen yada labarai. kafin malamin yace komai an samu wasu maluma na sunnah wadanda suka yi raddi na ilimi zuwa ga masu kalubalantar malamin game da gaskiyar da ya fada wacce maluman sunnah MA sun tafi akanta. Daga bisani shehin malamin shima ya tofa albarkacin bak...

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia ta gudanar da taro domin sanin makamar aiki

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia (MASISIJA) ta gudanar da muhimmin taro domin sanin makamar aikinta na yada da'awar maluman muslunci.  Ranar laraba 10/06/2020 wasu daga cikin jagororin wannan kungiya suka yi taro inda suka tattauna akan muhimman abubuwanda zasu taimaka masu a fagen aikinsu.  Watanni biyu da suka gabata kungiyar MASISJA ta shirya wata muhadara mai taken "Tambayoyi da Amsoshi" ta tsawon sati shidda (6) wadda Sheikh Barista Ibrahim Sabi'u Jibia ke gabatarwa.  A cikin ikon Allah,  an gabatar da ta tsawon makonni hudu (4) sai cutar Covid-19 ta billo wanda hakan yasa hukuma ta dakatar da dukkanin wani taro domin samun kariya daga cutar.  To Allah da ikonsa kuma bayan cutar ta lafa a jihar Katsina, yanzu an cigaba da harakoki kamar yadda aka saba.  Saboda haka ne kungiyar MASISJA, a karkashin wannan mitin, ta shirya tsaf domin cigaba da muhadarar tsawon sati biyu wadda mata ne kadai za ayi wa banda maza ka...

MA'ANAR SHI'A DA MANUFOFINSU (003)

Wannan raddi ne na uku zuwa ga Ado Lamama game da shirmenda yayi a matsayin raddi zuwa ga Malamin sunnah Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia. Daga: Sheikh Mustafa Mansur Jibia Ado  ya ce: Saed bn musayyib shima dan shia ne kuma shine shugaban masu tafsiri na tabi'ai. To ni kuma nace sam ba dan shia ba NE kuma ma karya ce shi ba malamin tafsiri ba NE,  ko da yake shi lamama bai fadi madogararsa ba, amma ni ku biyo ni ku ga tawa madogarar.  Saed bn musayyib dai haifaffen garin madina NE,  kuma tabi'i NE,  daya ne daga cikin maruwaita hadisin manzon Allah,  kuma daya daga cikin masana fiqhun madina guda bakwai daga cikin tabi'ai, anayi masa laqabi da babban malamin madina kuma shugaban tabi'ai. Idan mai karatu dalibin ilmi ne ko nan na tsaya zai fahinci lalle Saed bn musayyib sunni NE,  saboda kasancewarsa mutumin madina kuma mahaifinsa sahabi haka ma Kakansa. Bugu da kari acikin madina ne Ya kare rayuwarsa. Ga sahabbanda yayi karatu ...

MA'ANAR SHI'A DA MANUFOFINSU (002)

Raddi na biyu zuwa ga Ado Lamama game da shirmenda yayi a matsayin raddi zuwa ga Malamin sunnah Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia. Daga: Sheikh Mustafa Mansur Jibia  Ado ya ce: sayyidnah Aliyu dan shia  ne, ni kuma nace sam babu alaka tsakanin sayyidnah Aliyu da shia, Bal ma shi Ahlussunna NE. Madogarata itace: Manzon Allah ne da kansa yace sayyidnah Aliyu sunni ne ba shiey  ba. In da yake cewa:عليكم بسنتي وسنة الخلفاء الراشدين المهديين عضوا  عليها باالنواجذ.   Maana na horeku da rike sunnata da kuma sunnar khalifofina Shiryayyu kuma masu shiryarwa ku cijeta da hirorinku. Acikin wannan hadisi Wanda ya inganta kuma mashhurine ga bakunan musulmi Wanda bai bukatar takhriji, zamu fahinci Manzon Allah Ya kira khalifofinsa da cewa Ahlussunna NE, Wanda kuma sayyidnah Aliyu daya daga cikin khalifofin Annabi, to mi ya hada sayyidnah Ali da shia, balle har ace Idan ya bada ilmi an koya ne daga dan shia? Babu alaka tsakanin kare da Liman. Masu Saur...